1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Tsohon shugaban Côte d'Ivoire ya amince da tsayawa takara

March 11, 2024

An sake bude sabon babin siyasa a Côte d'Ivoire sakamakon amincewa da Laurent Gbagbo ya yi na tsayawa takara, duk da hukuncin daurin shekaru 20 da kotu ta yanke masa kamar yadda jam'iyyarsa ta fitar da sanarwa.

Tsohon shugaban Côte d'Ivoire Laurent Gbagbo a lokacin da ya bayyana a kotun Hague, inda ya ke gaisawa da magoya baya a harabar kotun.
Tsohon shugaban Côte d'Ivoire Laurent Gbagbo a lokacin da ya bayyana a kotun Hague, inda ya ke gaisawa da magoya baya a harabar kotun.Hoto: Jerry Lampen/AP/picture alliance

Gbagbo, wanda ya fuskanci hukunci a kotun hukunta manyan laifuka dake birnin Hague, ya shaki iskar 'yanci daga kotun a shekara ta 2019, duk da cewa kafin wannan hukuncin kotun Côte d'Ivoire ta yanke masa hukuncin daurin shekaru 20 sakamakon mallakar wasu bankuna ta hanyar halasta kudin haram.

Karin bayani: Gbagbo zai iya komawa gida - Ouattara 

Tsohon shugaban kasar ya gamu da tirjiya bayan ya fadi zaben 2010, ga Allasane Outtara, inda Gbagbon ya ke sauka daga mulkin wanda hakan ya haifar da tashin hankali a fadin kasar.

Karin bayani: Ouattara ya ce ba zai tsaya takara ba 

Babbar jam'iyyar adawar kasar ta Democratic Party of Ivory Coast (PDCI), ta nada Tidjane Thiam a matsayin shugaban jam'iyyar a watan Disambar bara, duk da cewa har yanzu babu tabbacin ko Thiam ko kuma  Alassane Ouattara  za su tsaya takara a babban zaben 2025.