Turai ta bukaci kawo karshen yamutsin Burundi
December 14, 2015![USA UN PK Mogherini Treffen Nahost-Quartett in New York](https://static.dw.com/image/18752403_800.webp)
Talla
Kimanin mutane 87 suka mutu a kasar ta Burundi bayan wasu hare-hare da 'yan tada kayar baya suka kai a kan wani barikin sojoji a ranar Jumma'a wadanda ake kyautata zaton masu adawa da tazarcen Shugaba Pierre Nkurunziza ne.
A yayin taron ministocin kasashen Turan da suke gudanarwa a birnin Brussels, kantomar harkokin wajen EU Federica Mogherini ta yi nuni da cewar:
Sun tuntubi shugabanin kungiyar Afrika da su shiga a dama da su wajen tattauna batun zaman lafiyar Burundi bisa jagorancin yankin.