Turai za ta karfafa dangantakar cinikayya da Afirka
March 10, 2020![Äthiopien Ursula von der Leyen Addis Ababa](https://static.dw.com/image/51567430_800.webp)
A watan Fabarairu ne shugabar hukumar Kungiyar Tarayyar Turai, Ursula Von der Leyen ta jagoranci tawagar kungiyar zuwa birnin Addis Ababa na kasar Habasha inda ake da hedkwatar Kungiyar Tarayyar Afirka, a zaman taron aka tattauna sabbin matakai na hadin gwiwa. Batu na farko shi ne samar da mafita a kan matsalar sauyin yanayi dama fasahar sadarwar zamani.
Batun masu neman mafaka a nahiyar Turai, wanda aka dade ana sukar lamirin Kungiyar EU na hana bakin haure daga nahiyar Afirka shiga Turai na daga cikin batutuwan da za a mayar da hankali a kai, amma tuni wakilan kungiyar suka kare kansu daga wannan zargi.
Gidauniyar Menschen für Menschen mai taimakon al'umma da ke Jamus na mai ganin akwai bukatar a sasauta al'amura don kar tarihi ya maimaita kansa.
Wani batu da ake kuma son ganin kungiyar ta mayar da hankali a kai, shi ne inganta rayuwar al'umar nahiyar ta Afirka musamman ma matasa da akasarinsu ke zaman kashe wando a sakamakon rashin aikin yi, ana ganin cewa su ne suka fi yawa a cikin al'umma akwai bukatar a tallafa musu don rage bara gurbi da ake kallo na asassa tashe-tashen hankula a sassan nahiyar.