1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Tattalin arziki

Belarus: Turkiyya ta rage jigilar fasinja

Lateefa Mustapha Ja'afar SB
November 12, 2021

Biyo bayan matsalin lamba daga kasashen kungiyar Tarayyar Turai EU, Turkiyya ta hana 'yan wasu kasashen Larabawa tashi daga kasarta zuwa Belarus.

Türkei Istanbul Airport Flugzeuge Turkish Airlines
Hoto: Agron Beqiri/NurPhoto/picture alliance

A yanzu dai mahukuntan na Ankara sun bayyana cewa ba za a kara barin wadanda ke dauke da fasfo din kasashen Siriya da Iraki da kuma Yemen su hau jirigin saman Turkiyya ba. A hannu guda suma mahukuntan na Belarus sun sanar da cewa tuni suka fara bin umurnin na Ankara, ta hanyar hana fasinjojin da abin ya shafa shiga jirgin sama mallakar kasar ta Belarus.

Tun da farko dai kungiyar Tarayyar Turan EU, ta yi barazanar kakaba takunkumi ga duk wani kamfanin jiragen sama da ya kwaso 'yan gudun hijira zuwa Belarus, da nufin ba su damar yin amfani da Minsk din domin shiga EU ba bisa ka'ida ba.