Bala'iKenya
Turmutsutsi wajen karrama gawar Odinga
October 17, 2025
Talla
Gomman mutane sun jikkata yayin wani turmutsutsi wajen zaman makoki na karramawa da aka yi wa gawar madugun adawa Raila Odinga a Nairobi babban birnin kasar Kenya.
Gidan talabijin din Kenya NTV ya wallafa wani hoto a shafin X jami'an agaji na bayar da kulawa ga wasu masu zaman makoki da suka sami raunuka.
Majiyoyi daga asibitoci sun ce an kwantar da akalla mutane 17 bayan turmutsutsin
Wannan na faruwa ne kwana guda bayan da jami'an tsaro suka bude wuta kan mai uwa da wabi domin tarwatsa dandazon masu makoki inda suka kashe akalla mutane uku.