1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Annobar corona za ta hana yara karatu

Abdoulaye Mamane Amadou
September 3, 2020

Hukumar 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, ta bayyana cewa rashin daukar kwararan matakan dakile coronavirus ya yi illa ga karatun miliyoyin yara 'yan gudun hijira a duniya.

Gazastreifen Schule UN Flüchtlingslager Al-Shati
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Talatene

Babban jami'in hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya Filippo Grandi, ya ce bayan yanayi na mawuyacin halin da suka fuskanta a baya, bai dace a hanasu samun ingantacciyar makoma ba a yanzu saboda haka ya bukaci a dage don basu ilimi.

Hukumar kula da 'yan gudun hijirar dai na fargabar makomar yaran ne duk da abinda zai biyo bayan karshen annobar Corona, inda ta ke hasashen mafi yawancinsu za su dakatar da zuwa makaranta bisa fuskantar wasu tarin matsaloli na rayuwa ciki harda na daukar dawainiyar karatunsu da na iyali.