1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

UNICEF: An wulakanta yara a duniya

December 28, 2018

Majalisar Dinkin Duniya, ta ce rayuwar kananan yara ta fuskanci tsananin barazana a wannan shekarar da ke ban kwana, musamman a wuraren da ke fama da rikice-rikice a fadin duniya. 

Südsudan - Kindersoldaten
Hoto: Getty Images/AFP/C. Lomodong

Asusun kula da yaran na kasashen duniya UNICEF, ya ce daga watan Janairu zuwa yanzu, bangarori masu rikici a duniya sun yi ta yi wa rayuwar yara galatsi mai munin gaske.

Asusun ya lasafto kasashe irin su Siriya da Yemen da Kwango da Najeriya da Sudan ta Kudu, a matsayin kasashen da matsalar ta fi kamari a cikinsu.

A kasar Myanmar an yi wa yara da dama fyade da auren dole, a cewar UNICEF, yayin da a Afghanistan yara kimanin dubu biyar aka kashe, sai kuma a Somaliya da aka tilasta wa 1,800 shiga aikin soja.

Majalisar ta Dinkin Duniya ta ce tilas ne a sama wa matsalar magani cikin gaggawa.