UNICEF: Rikicin Gabas ta Tsakiya na hallaka yara
February 5, 2018![UNICEF Foto des Jahres](https://static.dw.com/image/41902639_800.webp)
Talla
Asusun kula kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya ce watan Janairun 2018, ya kasance bakar wata ga kananan yara ganin yadda aka zubda jinin yara a kasasahen Iraki da Siriya da Falatsinu da Yemen da kuma Libiya.
UNICEF ta ce ba za a bari jinin yaran ya bi ruwa ba, wajibi a su taimaka a daga muroyoyin wadanda ba hali su bayyana kukansu. A don haka suke kira da a kawo karshen afkawa kananan yara a lokutan yaki.
Wasu alkaluma da MDD ta wallafa ya nuna cewa an kashe kananan yara 59 a Siriya, yayin da kasar Yemen ke biyemata cikin kashen da akafi salwantar da rayuwar yara.