Ursula von der Leyen za ta sake neman shugabancin EU
February 19, 2024![](https://static.dw.com/image/68282847_800.webp)
Shugabar hukumar zartarwa ta Kungiyar Tarayyar Turai Ursula von der Leyen za ta halarci taron kwamitin zartarwa na CDU a Berlin a wannan Litinin.
Wakilan jam'iyyar na sa ran von der Leyen ta ayyana aniyarta ta sake tsayawa takara a karo na biyu a shugabancin hukumar ta EU.
Karin bayani:Majalisar EU na shirin bai wa Von der Leyen damar zarcewa
Daga nan ne jam'iyyar CDU za ta gabatar da 'yar takarar mai shekaru 65 da haihuwa a matsayin babbar 'yar takarar jam'iyyu masu ra'ayin rikau na Turai (EPP) a zaben Turai da za a yi a watan Yuni.
Karin bayani:EU: Sake gina Ukraine da kudaden Rasha
Sai dai mambobi za su yanke shawara a taron gamayyar jam'iyyun da ke da ra'ayin rikau EPP a ranakun 6 da 7 ga Maris a Bucharest babban birnin kasar Romaniya. Tsohuwar ministar tsaron Jamus von der Leyen ta kasance shugabar hukumar zartarwar ta EU tun 2019.