Venezuela ta dangana da samun kujerar komitin Sulhu
October 25, 2006Bayan taci-bata ba taci ba,da aka sha yi ,a zaɓen raba gardama, tsakanin ƙasashen Venezuella, da Bolivia, a takara kujera komitin sulhun Majalisar Ɗinkin Dunia, a ƙarshe Venezuela, ta dangana, da samun wannan matsayi.
Sanarwar ta hito daga fadar shugaban ƙasar Bolivia, Evo Morales.
Idan dai ba a manta ba , an yi zaɓe har zagaye 35, a makon da ya gabata, domin hida gwani tsakanin ƙasashen 2, domin wakiltar yankin Latine Amurika, a komitin sulhu na Malalisar Ɗinkin Dunia, ba tare da an cimma nasara ba.
Sakamakon ƙuri´un, a ko da yaushe, na jera ƙasashen 2 a kunnen doki.
Nan gaba a yau, Majalisar Ɗinkin Dunia ke kaɗa sabuwar ƙuri´a, karo na 36.
To saidai ya zuwa yanzu, ƙasar Venezuela, da Amurika ta azawa karan tsana, ba ta hito hili ba, ta gaskanta sanarwar janyewar ta daga samun wannan kujera.