1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Adadin wadanda suka mutu a jihar Filaton Najeriya na karuwa

December 27, 2023

Jerin hare-haren da wasu dauke da makamai suka kai kauyukan jihar Filato a tsakiyar Najeriya ya doshi 200 a cewar hukumomi. Harin ya faru ne a karshen makon jiya.

Yadda ake kwashe gawarwakin mamata bayan hare-hare a arewacin Najeriya
Hoto: Stringer/REUTERS

Adadin wadanda suka mutu a jerin hare-haren da 'yan bindiga suka kaddamar a kan wasu kayukan jihar Filato a Najeriya a karshen mako, ya kai kusan mutum 200 a halin yanzu.

Hare-hare ne da suka faro daga yankin karamar hukumar Bokkos da yammacin ranar Lahadi, inda kuma ya dangana da karamar hukumar Barikin Ladi.

Jagoran karamar hukumar Bokkos, Monday Kassah ya ce mutane 148 ne aka kashe a lamarin jimilla, yayin da Dickson Challom wani zababben dan majalisa daga yankin Barikin Ladi, ya tabbatar da cewa maharan sun kashe mutane 50.

Akwai ma wasu daruruwan mutanen da 'yan bindigar suka jikkata a hare-haren a cewar mahukunta.

Kungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International dai ta zargi gwamnatin Najeriya da rashin daukar matakan da za su kawo karshen kare-kashe da ake yi a yankunan karkara a jihar Filato.