1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Lafiya

Iran: WHO ta dakatar da babbar cibiyarta a Dubai

March 5, 2026

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta dakatar da cibiyarta ta rarraba kayan agajin gaggawa a Dubai saboda barazanar hare-hare a yankin Gulf, lamarin da ka iya jinkirta tallafin lafiya ga kasashe da dama.

Shugaban hukumar WHO Adhanom Ghebreyesus
Shugaban hukumar WHO Adhanom GhebreyesusHoto: Denis Balibouse/File/REUTERS

Shugaban hukumar Dr. Tedros Adhanom Ghebreyesus ya bayyana a wannan Alhamis cewa dakatarwar ba ta shafi kasashen da abin ya faru kusa da su kawai ba, domin cibiyar na taka muhimmiyar rawa wajen tallafawa harkokin lafiya na gaggawa a duniya baki daya.

Karin bayani: Tasirin yakin Iran kan alakarta da Afirka
 

Daraktar WHO mai kula da yankin Gabashin Bahar Rum, Hanan Balkhy, ta ce cibiyar Dubai ta kula da rarraba kayan agajin gaggawa guda 500 da aka aika zuwa kasashe 75 a shekarar da ta gabata.

Ta kara da cewa rikicin da ke faruwa yanzu ya hana kaiwa ga kayan tallafin lafiya na kusan dala miliyan 18, yayin da wasu kaya na darajar dala miliyan 8 ma ba su iya isa cibiyar ba.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW