1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Al'ummar Gaza na mutuwa wajen karbar biredi da ruwa-Erdogan

July 22, 2025

Shugabannin kasashe da gwamnatoci na ci gaba da kiraye-kirayen tsagaita bude wuta a yankin zirin Gaza, wanda ke karewa a kan fararen hula.

Dandazon mata a lokacin da suke rububin karbar abinci a birnin Khan Younus na Gaza
Dandazon mata a lokacin da suke rububin karbar abinci a birnin Khan Younus na GazaHoto: Abed Rahim Khatib/Anadolu/picture alliance

Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya yi magana da kakkausar murya a birnin Santanbul, inda ya ce al'ummar Gaza ba za su ci gaba da mutuwa a wajen rububin karbar abinci ba.

Karin bayani:Erdogan ya nemi a kakaba wa Isra'ila takunkumi kan makamai

Kalaman Erdogan na zuwa a daidai lokacin da shugabannin kasashe da gwamnnatoci ke ci gaba da kiraye-kirayen tsagaita bude a wuta a yankin Zirin Gaza, kusan a kowacce rana Isra'ila na kashe fararen hula musamman mata da kananan yara a wajen turmutsitsin karbar abinci.

Karin bayani:Turkiyya ta bukaci Amurka ta sa baki don tsagaita wuta a Gaza

Babbar Jami'ar Diflomasiyyar EU Kaja Kallas ta sake jaddada matsayar Tarayyar Turai na kawo karshen halaka fararen hula a Gaza. Ta kara da cewa ta tattauna da Ministan Harkokin Wajen Isra'ila Gideon Saar kan bukatar dakatar da yakin da kuma shigar da kayan agajin jinkai Gaza.