Yadda jaridun Jamus ke kallon rawar Afirka a yakin Iran
March 6, 2026
Jaridar Frankfurter Allgemeine Zeitung ta wallafa sharhi game da tasirin yakin Iran na yankin Gabas ta Tsakiya kan kasashen Afirka. Ta ce yawancin kasashen Afirka na da kyakyawar hulda har ta cinikayya da kasahen, amma tun lokacin da aka fara yakin Iran, kasashe kalilan ne suka fito suka nuna takaicinsu saboda suna jin tsoron shugaban Amurka Donald Trump.
Wasu sun fito sun suna Amurka inda suka yi Allah wadai a kan hare-hare da ta kai, wasu kuma kasashen na yin suka a kaikaice ba tare da bayyana suna ba. Misali, shugaban Afirka ta Kudu wanda dama huldar kasarsa da Amurka ke tangal-tangal, na fatan samun ragewar kudaden harajin a kasuwanci tsakanin kasarsa da Amurka.
Shugaban Afirka ta Kudun ya yi likimo ya saka wa bakinsa linzami a kan yakin Amurka Israila da Iran, musammun ganin yadda Iran da Afrika ta Kudu suke cikin kasashen BRICS amma shugaba Cyril Ramaphosa, ya gaza cewa komai, Sai dai ya bayyana wata sanarwa ba tare da ambato sunan Amurka ko Isra'ila ba. Jaridar ta ce baya ga shi, kasashen Afirka da dama da ke da hulda da Iran sun yi shuru saboda jin tsoron Trump
Nitsewar jirgun ruwa a Kasar Libiya
Sai jaridar Die Tageszeitung wacce ta wallafa sharhinta mai taken wani jirgin ruwan Rasha mai suna LNG ya nitse a gabar tekun Libiya bayan tarwatsewarsa. Jaridar ta ce da alama Ukraine ta kai hari kan wanan jirgin ruwan Rasha da jirgin sama marasa matuki. Amma bayan fashewa da gobara mai tsanani, jirgin ya nitse tsakanin Libiya da Malta.
Jirgin yana dauke da iskar gas mai gurbata muhalli kuma ya tashi daga Murmansk a arewacin Rasha. Jirgin ruwan yana aikin safarar man fetur na Rasha da Iran da Venezuela, wanda zuwa kashi 80% na fitar da man fetur na Rasha ana sarrafa su ta wannan hanyar. Daruruwan irin wadannan jiragen na cikin jerin takunkumin kasashen Yamma.
Kungiyar M23 na ta'asa a Kwango
A sharhin jaridar Zeit Online, ta yi tsokaci a game da mutuwar mutane 200 a rugujewar mahakar Coltan a gabashin Kwango wacce ta ce wani iftala'in ya sake faruwa a mahakar Rubaya a gabashin Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango. 'Yan tawayen M23 sun musanta alkaluman gwamnati kan adadin wadanda suka mutu. Ruguzawar ta faru ne a mahakar Rubaya, wadda kungiyar 'yan tawayen ta M23 ke iko da ita.
Kungiyar M23 ta musanta labarin gwamnatin Kwango game da lamarin Fanny Kaj, wani mai magana da yawun 'yan tawaye ya ce mutane biyar ne kawai suka mutu. Sannan ya ce babu zaftarewar kasa.
Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ce kasar da ke kan gaba a duniya wajen samar da ma'adinin coltan wanda ake bukatarsa wajen kera wayoyin hannu na zamani da na'ura mai kwakwalwa da injunan jiragen sama. A cewar binciken wata hukuma ta Amurka (USGS), Kwango ta samar da kusan kashi 40% na ma'adinin coltan na duniya a shekarar ta 2023.