1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Yakin Iran na fadada

Suleiman Babayo AH
March 30, 2026

Ana ci gaba da neman hanyoyin warware yakin da ke faruwa a Iran da kasashen Amurka da Isra'ila.

Kasar Iran sakamakon hare-haren Amurka da Isra'ila
Kasar Iran sakamakon hare-haren Amurka da Isra'ilaHoto: Majid Asgaripour/WANA/REUTERS

Shugaban majalisar gudawawar Tarayyar Turai, Antonio Costa ya yaba da tattaunawa ta wayar tarho tare da Firaminista ‌Shehbaz ⁠Sharif ⁠na kasar Pakistan, kan batun samar da mafita na kawo karshen yaki a Iran, bayan kasashen Amurka da Isra'ila sun kaddamar da farmaki kan kasar.

Tattaunawa

Ita dai Pakistan ta karbi taron ministocin harkokin wajen kasashen Masar da Saudiyya, da Turkiyya a birnin Islamabad na kasar ta Pakistan.

Wannan na zuwa lokacin da Iran take cewa wuraren tarhi na kasar kimanin 130 aka lalata sakamakon hare-haren kasashen Amurka da Isra'ila. A birnin Tehran fadar gwamnatin Iran kadai kimanin wuraren tarihi 61 aka lalata a cewar gwamnatin kasar.