1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yakin neman zabe a kasar Gabon

November 24, 2005

Ranar lahadi ce mai zuwa idan Allah ya kai mu, a ke shirya zaben shugaban kasa a Gabon.

A halin da ake ciki jam´iyu daban daban na ci kin yakin neman zabe, saidai masu kulla da a al`ammuran siyasar a kasar sun tabbatar da cewa, babu shaka Shugaba Omar Bango za shi tazarce a wannan mukami.

Omar Bango na da shekaru 28 daidai bisa karagar mulkin kasar Gabon, idan a ka zabe sa ranar 27 ga watan nobemba, zai kara wasu shekaru 7.

Jam´iyun adawa sun zargi shugaban kasar, da anfani da dukiyar jama´a, a cikin yakin neman zabe.

Kamar yadda dokoki su ka tanada a Gabon, zagaye daya kawai a keyi a zaben shugaban kasa, matakin da ke kara tabatar da shugaba mai ci yanzu za shi tazarce.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW