1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fargaban MDD a kan yakin Sudan

Abdourahamane Hassane
May 23, 2023

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta damu game da barazanar da yakin Sudan kan iya haddasa wa zamantakewar al'umma wadanda ke da rarrabuwar kawuna a kan yakin.

Sudan Unruhe Konflikt
Hoto: AFP via Getty Images

Manzon musammum na MDD a Sudan Volker Perthes ya shaida wa kwamitin sulhu na MDD cewar yana da fargabar kan yakin da ake yi a Sudan ya rikide ya koma na kabilanci. Volker ya ce a wasu sassan kasar, yakin da ake yi tsakanin sojojin ya sake farfado da rikicin kabilanci tsakanin al'umomin.Tun a ranar 15 ga watan Afrilu, yakin da ake gwabza tsakanin sojojin Janar Abdel Fattah al-Burhane da na dakarun rundunar daukin ggagawa ta  FSR  na Janar Mohamed Hamdane Daglo ya yi sanadin mutuwar duban rayuka tare da raba sama da miliyan guda da muhallansu.