1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Yamen: Mutane 53 sun kwanta dama

Abdoulaye Mamane Amadou
April 10, 2021

An hallaka mutane 53 a yayin wani batakashi tsakanin 'yan tawayen Hutis da dakarun da ke biyayya ga gawamnati a tsaunukan Kassara da Machjaa mai nisan kilo 120 daga birnin Sanaa.

Jemen | Huthi Rebellen
Hoto: Getty Images/AFP/G. Noman

Wata majiya ta shedawa kamfanin dillancin labaran AFP da cewar an shafe sa'o'i 24 ana dauki ba dadi a tsaunukan da ke arewacin Mareb, yankin da kuma Allah ya albarkata da dimbin arzikin man fetur, wanda tun a cikin watan Febrairu mayakan Hutis ke neman karbe iko da shi daga hannun sojan gwamnati.

Wannan lamarin na zuwa ne kwanaki bayan bangarori a wannan yanki, na ta linka kira da a tsagaita wutsa tsakanin kawancen sojan da Saudiya ke jagoranta da 'yan tawayen Hutsi masu masun goyon bayan Iran.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW