Zimbabuwe: Zanga-zangar adawa a Harare
August 16, 2019
Talla
Masu gangamin na zargin gwamnatin mai ci da zaluncin da ya shige na hambararriyar gwamnatin Robert Mugabe da ta gabata.
'Yan adawar dai sun yi gangami a dandalin taro da ke birnin Harare, domin kokawa da halin kaka-ni-ka yi da tattalin arzikin kasar ke ciki.
Tun da farko kotun kasar ta haramta gudanar da gangamin, a yayin da aka girke jami'an tsaro a sassa daban daban na babban birnin Zimbabuwe.
Sai dai babbar jam'iyyar adawar kasar ta yi kira ga mayo bayanta dasu kauracewa gangamin, saboda gudun zubar da jini.