'Yan adawar Siriya za su shiga tattaunawa
November 24, 2017![Riad Treffen Syrische Opposition Mistura](https://static.dw.com/image/41509690_800.webp)
Wata sanarwa da kungiyoyin suka fitar na cewa za su aike da wakilai 50, da za su halarci taron Majalisar Dinkin Duniya kan zaman lafiya da zai gudana a birnin Geneva.
Matakin kungiyoyin ya zo ne yayin da suke ganawa a birnin Riyadh na kasar Saudiyya, da nufin cimma matsaya gabannin ganawa da shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad a ranar 28 ga watan Nuwamba.
Cimma shawo kan kungiyoyin Siriyar ya samu nasara ne a kokarin masu shiga tsakanin na kasa da kasa, da ke kokarin kwantar da wutar rikici tsakanin 'yan adawa da bangaren gwamnati.
A baya dai MDD ta sha shirya tattaunawa da bangarorin biyu amma yana rugujewa. Yakin basasa a Siriya ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula sama da dubu 330,000, tare da tilasawa miliyoyin 'yan kasar tserewa matsugunansu.