Rikice-rikice
'Yan bindiga sun halaka mutane 40 a Haiti
August 25, 2026
Talla
Magajin garin Kenscoff ya ce maharan sun kutsa cikin sansanin da ke cocin a daren Lahadi, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama, yayin da suka yi garkuwa da wasu. Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin wadanda suka mutu zai iya kaiwa 47, yayin da sama da 22 suka jikkata.
Karin bayani : 'Yan bindiga sun bude wuta kan jirgin MDD a Haiti
Gwamnatin Haiti ta yi Allah-wadai da harin tare da tura karin jami'an tsaro yankin. Haiti dai ita ce kasa mafi talauci a nahiyar Amurka kuma tana fama da karuwar hare-haren kungiyoyin masu dauke da makamai, lamarin da ya raba kusan mutane miliyan 1.5 da muhallansu.
Karin bayani : Chad za ta aike da dakaru 750 zuwa Haiti don taimakawa tsaro