1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan bindiga sun kai harin da ya yi ajalin mutane a Katinsa

Abdoulaye Mamane Amadou
February 3, 2026

Garin Doma na karamar hukumar Faskari a jihar Katsina, wasu 'yan bidniga sun kai harin ramuwar gayya, tare da ajalin mutane 20 da yammacin ranar Talata

Sojojin Najeriya a cikin shirin ko ta-kwana
Sojojin Najeriya a cikin shirin ko ta-kwanaHoto: Sunday Alamba/AP/picture alliance

Bayannai daga kauyen Dona na karamar hukumar Faskari a jihar Katsina, sun tabbatar da cewa wasu mahara sun kai farmakin da ya kashe mutane akalla 20 a kauyen, da ke cikin karamar hukumar Faskari da yammacin ranar Talata.

Shugaban hukumar hukumar Surajo Aliyi Daudawa ne ya tabbatar da hakan a tattaunawarsu da wakilinmu Yusuf Ibrahim Jargaba inda yace harin na ramuwar gayya ne, to amma sai yanzu haka al'ummar yankin na Doma sun shiga rudani inda suke neman daukin mahukunta