'Yan bindiga sun kai harin da ya yi ajalin mutane a Katinsa
February 3, 2026
Talla
Bayannai daga kauyen Dona na karamar hukumar Faskari a jihar Katsina, sun tabbatar da cewa wasu mahara sun kai farmakin da ya kashe mutane akalla 20 a kauyen, da ke cikin karamar hukumar Faskari da yammacin ranar Talata.
Shugaban hukumar hukumar Surajo Aliyi Daudawa ne ya tabbatar da hakan a tattaunawarsu da wakilinmu Yusuf Ibrahim Jargaba inda yace harin na ramuwar gayya ne, to amma sai yanzu haka al'ummar yankin na Doma sun shiga rudani inda suke neman daukin mahukunta