1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

'Yan bindiga sun kashe mutane 200 a Najeriya

February 5, 2026

A jihar Kwara adadin mutanen da 'yan ta'adda suka kashe ya kai 162, baya ga jihohin Katsina da Benue da ke fuskantar barazanar tsaro.

Takalman wasu daga cikin wadanda 'yan bindiga suka sace a Najeriya
Takalman wasu daga cikin wadanda 'yan bindiga suka sace a NajeriyaHoto: KOLA SULAIMON/AFP

Dan Majalisar Tarayya da ke wakiltar yankin Mohammed Omar Bio, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa adadin mutanen da 'yan bindigar suka kashe a kauyukan Woro da Nuku ya kai mutum 162, wanda ke kasancewa hari mafi muni da aka gani a yankin.

Karin bayani:Harin da aka kai a Woro na jihar Kwara ya kashe mutane 67 

Gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana kaduwarsa dangane da wannan mummunar hari na ranar Talata, wanda ya bayyana shi a matsayin dabbanci.

Karin bayani: 'Yan bindiga sun kashe mutane a coci a Najeriya

Sakataren Kungiyar Red Cross a jihar ta Kwara, Ayodeji Emmanuel Babaomo, ya ce har ya zuwa wannan lokaci sun kasa isa yankin domin kai agajin gaggawa, sakamakon rashin kyawun hanya da kuma tazarar da ke tsakanin yankin da babban birnin jihar Ilorin. Kauyukan na Woro da Nuku dai na kusa da kan iyakar Najeriya da Jamhuriyar Benin.