Kwango ta sa dokar hana fita
May 2, 2021![DR Kongo Provinz Ituri | MONUSCO- Friedenstruppen](https://static.dw.com/image/54985322_800.webp)
Talla
'Yan bindiga dadi sun kashe akalla mutane 19 ciki har da sojojin gwamnati 10 a wasu tagwayen hare-hare da suka kaddamar kan kauyuka biyu a gabashin kasar.
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya Unicef, ya ce rikici da ke faruwa a gabashin kasar ya tsananta halin rayuwa bayan tilasta sama da mutane miliyan daya da rabi gudun hijira, wasu miliyon biyu na cikin tsananin bukatar gajin gaggawa.