1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan bindiga sun sace 'yan makaranta 25 a Najeriya

November 17, 2025

'Yan bindigan sun kuma halaka mutum daya tare da raunata daya yayin harin na ranar Litinin da Asuba.


Wani jami’in makaranta guda ya rasa ransa, yayin da wani kuma ya ji rauni a lokacin harin na 'yan bindigan
Wani jami’in makaranta guda ya rasa ransa, yayin da wani kuma ya ji rauni a lokacin harin na 'yan bindiganHoto: Haidar Umar/AFP

Wasu ‘yan bindiga sun sace mutane 25 tare da kashe wani ma'aikaci, a wani mummunan hari da suka kaddamar a wata makarantar sakandaren ‘yan mata a arewa maso yammacin Najeriya.

Rundunar 'yan sandan Najeriyar ta ce harin ya auku ne da misalin karfe hudu na asuba a makarantar sakandare ta mata mai suna Government Girls Comprehensive Secondary School da ke karamar hukumar Danko-Wasagu a jihar Kebbi.

Najeriya: 'Yan bindiga sun yi garkuwa da daliban jami'a

Harin yazo ne sama da shekara goma bayan sace kusan dalibai mata 300 na Chibok a yankin arewa maso gabashin kasar lamarin da ya jawo suka daga sassan duniya daban-daban.

Har ila yau, 'yan sandan sun ce 'yan bindigan sun rika harbe-harbe domin razana mutane da suke kusa da wajen saboda kar su kai dauki.

Wani jami’in makaranta guda ya rasa ransa, yayin da wani kuma ya ji rauni a lokacin harin na 'yan bindigan.

'Yan matan Chibok: Alhinin cika shekaru 10 da sace su

Yankin arewa maso yammacin Najeriya ya jima yana fama da ta’addanci daga ‘yan bindiga wadanda ke satar shanu da kuma mutane a kauyuka harma da kashe mutane ba gaira ba dalili.