'Yan gudun hijira na ƙasar Somaliya na cikin wani mawuyacin hali
July 19, 2011![](https://static.dw.com/image/15218683_800.webp)
Talla
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya wato HCR ,ta ce kaso na addadin waɗanda ke mutuwa na yan gudun hijira na ƙasar Somaliya a ƙasar Habasha.Ya ƙaru galibi yara ƙanana saboda rashin abinci mai gina jiki . wani jami'in hukumar Paul Spiegel ya ce lamarin ya ƙazance a sansani yan gudun hijira na garin Dolo Ado:
Inda yara yan ƙasa da shekaru biyar ke mutuwa ba ƙaƙautawa;mutane kimanin miliyion goma sha biyu ne a yankin na kusurwar Afirka ke fama da matsalar yuwan;a sakamakon farin da ake fama da shi wanda ya shafi ƙasashen Djibouti da Kenya da Habasha da kuma Yuganda .
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Eidita : Ahmad Tijani Lawal