Yan gudun hijira sun fara komawa gida a birnin Mogadiscio
May 11, 2007Talla
Hukumar Majalisar Ɗinkin Dunia mai kulla da yan gudun hijira ta ce mutanen da su ka tsere daga gidajen su, a sakamakon yaƙin da ya ɓarke a birnin Modasiscio na ƙasar Somalia, sun fara komawa gida.
Saidai wasu da dama kuma sun ce, su da Mogadiscio haihata-haihata, inji ƙungiyar, ta la´akari da tosran da ya kama zukatan su, na sake ɓarkewar wani saban rikici.
A jimilce, mutane dubu 400 su ka ƙauracewa Mogadiscio, domin tsira da rayukan su.
A wani labarin kuma ƙungiyar bada agaji ta Care Intrenational, ta nunar da cewa, ma´aikatan ta 2, da aka yi garkuwa da su a ƙasar ta Somalia,tun ranar laraba da ta wuce, su na cikin ƙoshin lahia.
Ƙungiyar ta shiga tantanwa, domin samun belin wannan ma´aikata.