1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan kasar Guinea-Bissau na zaben shugaban kasa

November 23, 2025

A wannan Lahadin ce, al'ummar Guinea-Bissau za su kada kuru'ar zaben shugaban kasa bayan kammala gangamin neman zabe na tsawon makwanni uku cikin lumana.

Shugaban Guinea-Bissau, Umaro Sissoco Embaló  da babban abokin hamayyarsa Fernando Dias
Shugaban Guinea-Bissau, Umaro Sissoco Embaló da babban abokin hamayyarsa Fernando DiasHoto: picture alliance | DW

A kalla masu kada kuri'a ne 860,000 ne za su zabi gwaninsu a cikin 'yan takara 12 a zaben kasar ta yammacin Afirka da ta fuskanci rikice-rikicen siyasa a baya, ciki har da yunkurin juyin mulki sau da dama. Ana hasashen cewa ta yiwu, shugaban kasar mai ci, Umaro Sissoco Embalo mai shekaru 53 ne ya iya lashe zaben da ake sa ran samun sakamako a hukumance zuwa nan da ranar Alhamis din mako mai zuwa.

Karin bayani:Shugaban Guinea-Bissau ya sanar da ranar yin zaben majalisa 

Shugaban zai kara ne da babban abokin hamayyarsa, Fernado Dias da ke samu goyon bayan babbar jam'iyyar adawa ta PAIGC da aka haramta wa shiga zaben. 'Yan kasar na fatan sabon shugabancin ya samar da karin ababen more rayuwa ga 'yan kasa da karin ayyuka domin magance talauci da cin hanci da kuma ta'amulli da miyagun kwayoyi.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW