1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

'Yan Malawi na zaben sabon shugaban kasa

Suleiman Babayo MAB
September 16, 2025

'Yan takara 17 cikin har da shugaban kasar Malawi na fafatawa kan neman shugabancin kasar da ke yankin kudancin Afirka mai fama da matsalolin tattalin arziki. Zaben ya kunshi na 'yan majalisa da kananan hukumomi.

Malawi Lilongwe 2025 | Zaben kasar Malawi na shekara ta 2025
Zaben kasar Malawi na shekara ta 2025Hoto: Amos Gumulira/AFP

'Yan kasar Malawi na kada kuri'a a zaben da Shugaba Lazarus Chakwera yake neman wa'adi na biyu na mulkin karin shekaru biyar.

Akwai 'yan takara 17 da suka fafata zaben ciki har da mutumin da shugaban ya gada tsohon Shugaba Peter Mutharika wanda shi ne babban babban mai kalubalantar shugaban.

Zabe cikin matsin tattalin arziki

'Yan takara a zaben MalawiHoto: Amos Gumulira/AFP/Getty Images

Ana zaben lokacin da kasar ke cikin matsi na tattalin arziki. Tsohuwar shugabar kasar Joyce Banda tana cikin masu fafatawa a zaben na yau Talata. Zanen ya kunshi na shugaban kasa da 'yan majalisa gami da na kananan hukumomi.

Kasar ta Malawi da ke yankin kudancin Afirka tana da mutane kimanin milyan 21, sannan akwai masu zabe kimanin milyan 7.2, kuma tana cikin kasashe 'yan rabbana ka wadata mu.