1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Dan adawar Zambiya na hannun 'yan sanda

Abdoulaye Mamane Amadou
August 27, 2026

Kafofin yada labarai na Zambiya sun ruwaito cewa madugun 'yan adawa kuma dan takarar jam’iyyar hamayya wanda ya zo na biyu a zaben shugaban kasar Brian Mundubile, yana hannun ’yan sanda kuma ana yi masa tambayoyi.

Madugun 'yan adawa Brian Mundubile lokacin da yake tattaunaw da DW a Lusaka
Madugun 'yan adawa Brian Mundubile lokacin da yake tattaunaw da DW a LusakaHoto: Kathy Short/DW

Jami'an 'yan sanda a Zambiya sun sanar da kama madugun 'yan adawan kasar Brian Mundubile, inda suke yi masa tambayoyi biyo bayan hargitsin da ya barke a zaben shugaban kasar da a gudanar a makon jiya. 

Zambia ta dakatar da sanar da sakamakon zabe

Gidan rediyon kasa na Zambiya, ya ce Mundubile da mutumin da ya yi masa takarar mataimaki Makebi Zulu sun shiga hannun hukuma, suna kuma yi musu tambayoyi.

Kakakin hukumar 'yan sandan Zambiya Godfrey Chilabi, ya sanar da cewar an saurari bayanai daga jagoran na 'yan adawa, game da zanga-zangar kin jinin sakkamakon zabe da ta barke a washe garin ranar zaben da babbar jam'iyyar da ke mulkin kasar ta yi nasara, sannan kuma za a fitar da sanarwa idan an kammala yi masa tambayoyi.

Yan Zambia sun yi zaben shugaban kasa

Mutum guda ne dai ya ce gagrinku, a yayin 'yan sanda suka cika hannu da membobi da dama na jam'iyyar ta madugun 'yan adawar, bisa boren kin jinin sakamakon da suka nuna a rranar 13 ga wannan Agusta.

Hukumomin Zambiya sun bayyana shugaba Hakainde Hichilema a matsayin wanda ya lashe zaben, duk da cewa an samu takaddama kan sakamakon.