1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sanda sun tsare masu bore a Hong Kong

Abdul-raheem Hassan
November 18, 2019

Bayanai na cewa 'yan sandan na barazanar amfani da harsasan gaske idan 'yan fafutukar tabbatar da dimukuradiyyar suka ki mika kai.

Hongkong Proteste
Hoto: Getty Images/A. Kwan

Rahotanni daga yankin Hong Kong na cewa 'yan sanda sun fesa hayaki mai sa kwalla tare da watsa ruwa zafi kan daruwan masu zanga-zanga da ke neman tserewa daga wata wata kwaleji, an dade ana zargin jami'an tsaron gwamnati na amfani da karfi kan masu boren, sai dai suna samun kariya daga gwamnati.

Wannan dai na zuwa a dai-dai lokacin da wata kotu a yankin na Hong Kong ta soke haramcin da aka yi na rufe fuska dan badda kama yayin gudanar da zanga-zangar neman 'yancin cin gashin kai daga gwamnatin Beijin.