'Yan tawaye sun kai hari kan soja a Mali
June 3, 2025
Talla
Kungiyar Jama'a Nusrat ul-Islam wa al-Muslimin watau JNIM a takaice, ta ce ta karbe iko da sansanin soji na Boulkessi da ke tsakiyar Malin, iyaka da Burkina Faso.
Sama da sojoji 30 ne dai suka salwanta a harin da sojoji suka ce an tilasta musu janyewa aka yi a lokacin.
Kungiyar ta JNIM ta kuma ma dauki alhakin hare-hare da dama a baya-bayan nan a yankin na Mali.
Ko a ranar 24 ga watan jiya ma dai ta ce ita ta kai hari a sansanin soji na Dioura inda sojoji 40 suka mutu.
A ranar Juma'a ma dai ta kwace wani sansanin na soji a Sirakorola a kudu maso yammaci, amma kuma dakarun kasar suka kwace.
Sama da sojoji 400 ne dai suka mutu a watan jiya sakamakon ayyukan ta'adda a kasashen Mali da Nijar da ma Burkina Faso.