Yarjejeniyar amincewa da sakamakon zabe
March 26, 2015![Nigeria Goodluck Jonathan Abdulsalami Abubakar Muhammadu Buhari](https://static.dw.com/image/18343564_800.webp)
Talla
Kimanin kwanaki biyu da a gudanar da zaben shugaban kasa a tarayyar Najeriya manyan jam'iyyun kasar biyu wato PDP da APC da kuma 'yan takarar da ke musu jagora sun dauki alkawarin mutunta sakamakon zaben komai daci. A wani taron da ya samu halartar manyan 'yan kwamitin tabbatar da sake zaman lafiya da safiyar wannan Alhamis a Abuja, shugaban Najeriya Goodluck Jonathan da kuma jagoran 'yan adawa Janar Muhammadu Buhari sun rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniyar tabbatar da zaben a cikin masalaha sannan kuma da amincewa da sakamakon da zai fito a cikinsa. A ranar Asabar za a gudanar da zaben da ake fargabar samun tashin hankali a cikinsa.