1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yau ICC za ta yanke hukunci game da yiwa Hissene Habre shari'a

July 20, 2012

Yau ne kotun hukunta laifukan yaƙi ta duniya za ta yanke hukunci ko ya kamata Senegal ta iza ƙeyar tsohon shugaban Chadi Hissene Habre domin yi masa shari'a.

Das undatierte Archivbild zeigt den Ex-Präsidenten des Tschad, Hissene Habre. Menschenrechtler in Afrika wollen Habre, den Ex-Machthaber des Sahelstaates Tschad, vor Gericht bringen. «Habre ist Afrikas Pinochet», sagte in Dakar Reed Brody von der internationalen Menschenrechtsorganisation Human Rights Watch. Während Habres Regierungszeit (1982-1990) sollen nach Angaben einer Wahrheitskommission 40 000 Menschen aus politischen Gründen ermordet und 200 000 gefoltert worden sein. Habre (57) lebt im Exil in der senegalesischen Hauptstadt Dakar. dpa (zu dpa 0007 vom 28.01.2000)
Hissene HabreHoto: picture-alliance/dpa

Harwayau, kotun za ta yanke hukunci ko ya kamata Mista Habre ya gurfana a ƙasar ta Senegal.

Ana zargin Mista Habre ne dai da laifin azabtarwa da kuma kisan dubun-dubatar masu adawa da shi lokacin da ya ke kan karagar mulkin ƙasar ta Chadi tsakanin shekara ta 1982 zuwa shekarar 1990 lokacin da soji su ka hamɓarar da shi daga karagar mulki.

A cikin shekara ta 2005 ne dai mahukuntan Belgium su ka shigar da ƙara gaban kotun bayan da wadanda gwamantin Mista Habren ta azabtar su ka gabatar da ƙorafinsu.

A yanzu haka dai tsohon shugaban yana zaman gudun hijira a ƙasar Senegal inda mahukuntan ƙasar ke masa ɗaurin talala.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Abdullahi Tanko Bala