Nijar: Yaushe za a sasanta da Orano?
February 4, 2026
Jamhuriyar Nijar din dai ta ce, a wannan tafiya shure-shuren da kamfanin na Orano ke yi ba zai hana masa mutuwa kan wannan batu. Shi dai wannan kwamiti da ministan shari'a da kula da 'yancin dan Adam da hulda tsakanin manyan ma'aikatu na Nijar Alio Daouda ya kaddamar, ya kunshi kwararru a fannin shari'a da muhalli da kiwon lafiya da kare hakkin dan Adam da kuma masana hakar makamashin uranium. Kwamitin zai dukufa wajen tattaro bayanai domin samar da cikakken kundi da zai kunshi duk kararraki da sauran ja-in-ja da ke tsakanin Nijar din da kamfanin Orano na Faransa.
Zargin Orano ga Nijar
Da yake magana kan zarge-zargen da kamfanin na Orano ke ci gaba da yi wa Nijar, ministan shari'ar ya ce akwai abubuwa da dama da 'yan kasar da ma sauran al'ummar duniya ba su sani ba kan wannan batu.Tuni masu sharhi kan harkokin shari'a kamar Dakta Atto Namaiwa da ke bibiyar wannan ja-in-ja tsakanin Nijar da Orano sau da kafa ya ce, yana da kyau wannan kwamiti ya bi diddigin abubuwan da yarjejeniya tsakanin Orano da Nijar ta kunsa, domin gudun kar a yi kitso kai cike da kwarkwata.
Wane zargi Nijar ke wa Orano?
A hannu guda kuma Nijar din ta zargi kamfanin na Orano da yin babban sakaci da ka'idojin kiyaye lafiya da muhalli, wanda a baya take cin karanta ba babbaka kan aikin na hakar uranium. Hukumomin na Nijar sun ce, sun bincika komai kuma ba su yarda da miyagun abubuwan da suka wakana tsawon shekaru ba. Kwamitin kwararrun, ya kunshi 'yan kungiyoyin farar hula masu kare hakin dan Adam da sauran masu sa ido kan albarkatun karkashin kasa da Nijar din ke hakowa.