Rahotanni daga yankin Zirin Gaza na Falasdinu, na nuni da cewa wasu 'yan jarida hudu na daga cikin mutane takwas din da suka hadu da ajalinsu a harin sojojin Isra'ila na asbitin Nasser da ke tsakiyar birnin Gaza.
'Yan jarida na cikin hadari a yankin Zirin Gaza na FalasdinuHoto: Stringer/REUTERS
Talla
Daga cikin 'yan jaridar da harin na Isra'ila ya halaka, har da Mariam Dagga da ke aiki da kamfanin dillancin labarai na Associated Press. Mai shekaru 33 a duniya, Dagga ce ta ruwaito labarin yadda likitoci a asibitin na Nasser ke fafutukar ceto rayuwar kananan yaran Zirin Gaza da yunwa ke nemana halaka su. Gidan talabijin din Al Jazeera ma ya tabbatar da rasuwar wakilinsa Mohammed Salam a wannan harin.
Gaza: Idan kida na tashi, sai a manta da yanayin yaki
A cikin buraguzan gine-ginen Zirin Gaza, matasan makada na rike da jita da sauran kayan kida. Suna samar da yanayi na fata da martaba, a daidai lokacin da ake fama da yunwa da rashi da kuma cutar tsananin firgici.
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
Hada hannu waje guda, domin yakar firgici
Kwalejin Gaza, makaranta a birnin Gaza. Harsashi ya farfasa bangon gine-ginen gidaje, yayin da tagogi suka tarwatse. A nan yara mata uku tare da namiji guda na zaune suna koyon kada jita, tare da malaminsu Mohammed Abu Mahadi. Malaminsu ya yi imanin kida zai taimaki lafiyar kwakwalen mazauna Zirin Gaza, daga firgicin tashin bama-bamai da zafin ciwuka da yunwa da rashin 'yanci.
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
Ci gaba da koyarwa
A farkon shekara ta 2024, Ahmed Abu Amsha malami ne da ke koyar da kidan jita da sauran kayan kida, ya kasance guda daga cikin malaman farko cikin malamai da daliban makarantar koyon kida ta Edward Said National Conservatory of Music da suka fara bayar da darasin koyon kida a yankin kudancin Gaza da yaki ya dai-daita. A yanzu ya sake komawa yankin arewacin birnin Gaza da zama.
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
'Kida na sanya mini kyakkyawan fata'
"Kida na sanya mini kyakkyawan fata da rage min firgici," a cewar Rifan al-Qassas mai shekaru 15 a duniya da ta fara koyon kidan (oud) wato jita ta gargajiya ta Larabawa tun tana shekaru tara. Al-Qassas na fatan kada jitarta a kasar waje. Al'umma na cikin fargabar kora daga Gaza, saboda matakin majalisar zartaswar Isra'ila na ranar takwas ga watan Agustan 2025 na kwace iko da yankin Zirin Gaza.
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
A cikin mafi munin yanayi
A gaban tantin malaman da ke koyar da kidan, akwai baraguzan gine-gine da suka rushe a birnin Gaza. Kusan gaba dayan al'ummar yankin na cikin tantunan gaggawa ne. Akwai karancin abinci da tsabtataccen ruwan sha da magunguna. Dalibai da malamansu na ba su da karsashi saboda yunwa. Wasunsu da kyar suke samun damar zuwa azuzuwansu.
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
Wani abu mai kyau da zai sassauta radadin mutuwa da wahalhalu
Bafalasdine Youssef Saad tsaye tare da jitarsa, a jikin ginin makarantar da yaki ya tarwatsa. Kayan kida kalilan ne suka tsira a rikicin. Tuni Youssef da ke da shekaru 18 a duniya, ke da babban fata: "Ina fatan zan iya koyar da yara kida, ta yadda za su ga haske duk da yanayin yaki."
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
Lokacin nuna basira
Duk mummunan yanayin da ake ciki, koyon kada kayan kade-kade na samun halartar 'yan kallo. Cikin tanti, daliban da ke koyon kidan na nuna kwarewarsu, yayin da 'yan kallo ke tafa musu. Kayan kidan na tashi, inda suke cimma dogon zango yayin da aka kada su. Mai shekaru 20 da ke koyon kidan jita ya bayyana cewa: "Ina son sanin sababbin salon kade-kade, musamman mai karfi, ina son kida mai amo.
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
Lokacin farin ciki
Waka ma na taka muhimmiyar rawa. Yadda muryoyin yaran ke tashi na da dadin sauraro, sabanin karar abubuwa masu fashewa da bama-bamai da ke yin kisa da al'ummar yankin Zirin Gaza suka saba ji yau da kullum.
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
Kida domin magance ciwo
Osama Jahjouh na busa sarewa da ake amfani da ita a kade-kaden Larabawa da Iraniyawa da kuma Turkawa. ya ce: "Wasu lokutan ina dogaro da salon horon numfashi ko kuma in zauna shuru ina busawa, idan karar habe-harbe da tashin bama-bamai suka yawaita. Idan ina yin busa, ina jin kamar zan iya sake yin numfashi, kamar sarewar na magance min ciwon da nake ji a cikin jikina."
Hoto: Dawoud Abu Alkas/REUTERS
Hotuna 81 | 8
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce, dan jaridarsa Hussam al-Masri ya halaka yayin da harin ya raunata dan jaridar Reuters din mai daukar hoto Hatem Khaled. Rundunar tsaron Isra'ilan IDF ta tabbatar da harin da ta kai a asibitin na Nasser da ke Khan Younis, tare da bayyana cewa ta yi da na sanin raunin da duk wani wanda bai-ji ba bai-gani ba ya samu kuma ba ta kai harin da nufin halaka 'yan jarida ba. Yakin Isra'la da Hamas dai, na zaman guda cikin wadanda suka fi lakume rayukan 'yan jarida, inda kawo yanzu 'yan jaridar 192 ne suka halaka a yankin Zirin Gaza na Falasdinu a yakin watanni 22.