1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaushe rikicin 'yan bindiga zai kare a Filato?

Abdullahi Maidawa Kurgwi ZMA
July 9, 2025

Jihar Filato dai ta sha fama da rigingimu na 'yan bindiga da kabilanci da na addini, lamarin da ke janyo hasarar rayuka da dukiyoyin al’umma.

Hoto: picture-alliance/dpa

Masana  harkokin tsaro a Najeriya sun kawo shawara cewa, ya kamata  gwamnatin  Filato ta horas da  jami'an tsaro 'yan sa-kai  wato Vigilante domin su  rika taimakawa wajen magance matsalolin tsaro da ke addabar jihar Filato. Wannan na zuwa ne yayin da ake ci-gaba da fuskantar hare haren 'yan bindiga da ke aukuwa a wasu  yankunan  jihar.

Jihar Filato dai ta sha fama da rigingimu na kabilanci da addini, lamarin da ke janyo hasarar  rayuka da dukiyoyin al'umma, Dangane da haka nema ake ci gaba da samun  shigar matasa cikin kungiyoyi sa-kai domin taimakawa wajen  magance wadannan nan  rigingimu. Ko shin  me ya sa aka kasa magance wannan matsala  ta jihar Filato. 

Tashin hankali na baya bayan dai shi ne  wanda ya  auku a tsakanin kauyukan Kukawa da Bunyum,  da ke  karamar  hukumar Kanem, kuma  rahotanni  sun  nunar da cewa an rasa rayukan  mutane da dama  yayin  arangama  tsakanin 'yan kungiyar sa-kai  ta vigilante na yankin.

Yanzu haka ma dai matasa da ke karamar hukumar Wase  wanda ke mawkabtaka da Kanem suma sun himmatu kokarin kare  yankinsu daga 'yan bindigar kasancewar a lokuta da dama mazauna kauyukan Wase na  fuskantar munanen hare hare  daga 'yan bindigar.  

Rundunar da ke wanzar da zaman lafiya a jihar  Filato ta yi karin haske kan lamarin inda cikin sanarwar da ta fitar ta hanun Kakakin ta  Major  Samson Nantip, ta ce mutane 8 ne aka kashe a  fito na fito tsakanin  'yan bindiga  da 'yan sa-kai a yankin  Kanem,  amma ba mutane 70 ba kamar yadda wasu kafofin labarai  ke   bayyanawa.