1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Ta'addanciMali

Mali: Yaushe zaman lafiya zai samu?

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 9, 2026

'Yan awaren Abzinawa a Mali tare da kawayensu masu alaka da kungiyar Al-Qaeda, sun kai hari kan ayarin motocin dakarun gwamnati da mayakan Rasha na Africa Corps a arewacin kasar.

Mali | Assimi Goïta | Rikici | Abzinawa
Shugaban gwamnatin mulkin sojan kasar Mali Assimi GoïtaHoto: ORTM/REUTERS

Kungiyar Azawad Liberation Front ta ce mayakanta sun kai harin ne a kusa da Tabankort, yayin da ayarin ke kan hanyarsa ta kai dauki ga sansanin sojoji da ke garin Anefis. Wata majiya ta tsaro a Malin ta tabbatar da cewa an yi wa ayarin kwanton bauna, kuma an ci gaba da gwabza fada.

Kungiyar FLA ta kuma yi ikirarin kwace iko da garin Anefis, duk da cewa mayakan Africa Corps da wasu sojojin Mali na ci gaba da rike sansanin sojojin da ke garin. Tun bayan juyin mulkin shekarun 2020 da 2021, gwamnatin mulkin sojan Mali na ci gaba da fuskantar kalubalen tsaro duk da alkawarin da ta dauka na dawo da zaman lafiya a kasar.