Yuganda da Ruwanda sun musanta batun 'yan gudun hijira
April 3, 2018![Washington Israle Min isterpräsident Netanjahu bei Pk mit Trump](https://static.dw.com/image/37572143_800.webp)
Talla
Tun da farko Firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana kin amincewarsa da shirin Majalisar Dinkin Duniya na kara tsugunar da 'yan gudun hijirar da suka fito daga Afirka a kasashen yammacin duniya a wannan Talatar, yayin da yake ganawa da wa su fusatattun jama'a mazauna kudancin birnin Tel Aviv.
A halin yanzu dai Netanyahu na fuskantar Allah wadai daga kungiyoyi daban-daban ciki kuwa har da jam'iyyarsa ta Likud mai mulki a kasar.