Yunkurin keta dokar ambaliya a Nuzilan
July 23, 2017Talla
Bayanan da ke fitowa daga kasar Nuzilan, na cewa mazauna wasu manyan biranen kasar da suka fusknaci bala'in ambaliya a 'yan kwanakin nan, na kokarin komawa gida, duk da kasancewar dokar ta-baci da gwamnati ta kafa. Daruruwan gidaje ne dai ambaliyar ta lalata a cikin makon jiya, sakamakon batsewar da wani kogi ya yi.
Sai dai bayanan na cewa akwai alamun janyewar ruwa, wanda kuwa shi ne sanadin yunkurin na komawa gida da mazaunan ke yi. Lamarin dai ya yi muni ne a biranen Christchurch da kuma Dunedin.