Yunkurin tallafawa wanda ke cikin matsi
December 8, 2014![Pressekonferenz Rücktritt Valerie Amos PK 16.11.2014 ARCHIV](https://static.dw.com/image/18090974_800.webp)
Talla
Shugabar hukumar bada agaji ta Majalisar Dinkin Duniya Valerie Amos ta ce za su batar da kusa rabin kudin da suke bukata ne kan wadandan yakin da ake yi a Siriya ya tagayyara duba da irin dimbin bukatun da suke da su.
Amos ta ce inda kudin sun samu, kusan mutane miliyan 60 ne a shekara mai kamawa za su amfana daga irin tallafin da za su bada daga cikin mutum miliyan 78 da ke warwaste a cikin kasashe 22.
To sai dai wannan tallafi da ake son badawa in kudin sun samu ba su hada da wanda ke cikin matsi a Djibouti ba da ma wanda rikici ya raba da muhallansu a yankin Sahel musamman tarayyar Najeriya da Mali, amma hukumar ta ce za ta nemi tallafi na musamman cikin watan Fabrairun badi don agaza musu.