Karancin cimaka ta mamaye kasashen Afirka
December 3, 2020
Talla
Kungiyoyin na zargin tashe-tashen hankula masu nasaba da rashin tsaro a kasashen musamman ma a yankin Arewacin Najeriya a matsayin kan gaba wajen hadasa karancin abincin, kana kuma muddin ba a dauki matakan da suka dace ba a gabanin karshen damanar badi, mutane akalla miliyan 24 ka iya fadawa cikin mummunar yunwa a yammacin na Afirka daga watan Yuni zuwa watan Agustan 2021.
Kasashen Najeriya da Burkina Faso ne ke kasancewa cikin tsananin yuwa a cewar kungiyoyin, sakamakon tsanantar da ake fuskanta na hare-haren 'yan bindiga da masu da'awar jihadi a cikin kasashen.