1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

WHO: Taron gaggawa kan cutar Coronovirus

Abdul-raheem Hassan
January 30, 2020

Hukumar lafiya ta duniya za ta yi ganawar gaggawa da domin tattauna yuwar ko za a ayyana dokar ta baci kan cutar numfashi da ke barazana ga rayuwar mutane a kasashe da dama.

Schweiz WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus
Hoto: AFP/F. Coffrini

Ya zuwa yanzu cutar Coronavirus ta halaka mutane akalla 170, sama da mutane 7,000 sun harbu da cutar tun bayan tabbatar da bullar ta a tsakiyar birnin Wuhan na China a karshen shekarar 2019.

Shugaban hukumar lafiya ta duniya Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce taron wajibi ne ganin yadda aka tabbatar da cutar a kasashen Jamus da Vietnan da Japan da wasu kasashen duniya da ke cikin ko ta kwana.