1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a kashe mutane 75 a Masar

July 28, 2018

Kotun kasar Masar ta yanke wa wasu mutane 75 hukuncin kisa, ciki har da shugabannin kungiyar nan ta 'yan uwa Mususlmi.

Ägypten | Massenverurteilungen mit 75 Todesurteilen für Anhänger der Muslimbruderschaft
Hoto: Reuters/A. A. Dalsh

Wata kotu a kasar Masar ta yanke wa wasu mutane 75 hukuncin kisa, ciki har da shugabannin kungiyar nan ta 'yan uwa Mususlmi ta Muslim Brotherhood da magoya bayansu.

Su dai mutanen an zarge su ne da gudanar da zanga-zanga da kuma zaman dirshen a shekara ta 2013, inda suka goyi bayan hambararren Shugaban Masar din Mohammad Morsi.

Wannan dai wani hukunci ne na wucin-gadi da mutum 739 ke fuskantar fushin doka.

Bayan hukuncin na yau Asabar, za kuma a mika batun ga babban Mufti na kasa don yanke hukuncin karshe, kamar yadda yake a tsarin dokokin Masar.

A ranar 8 ga watan Satumba ne kuma za a yanke wa wasu mutum 660 hukunci.