1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Indiya: Za a sake bude makarantu a Kashmir

Zainab Mohammed Abubakar
August 16, 2019

Gwamnatin Indiya ta tabbatarwa da kotun kolin kasar cewar, a ko wace rana tana nazarin matakin da ta dauka kan lardin Kashmir mai sarkakiya, kuma nan bada jimawa ba za a cire tsauraran matakan tsaro da aka sanya.

Bildergalerie Kaschmir Alltag in Srinagar
Hoto: Reuters/D. Ismail

Babban mai shari'ar kasar ta Indiya shi ne ya sanar da hakan a wannan Juma'ar, bayan da kotun kolin ta saurari karar kalubalantar matakin na gwamnati.

Wani jami'i a lardin na Kashmir ya sanarwa da manema labaru cewar nan ba da jimawa ba, za'a fara bude layukan tarho na gidaje da aka toshe, a yayin da makarantu zasu bude a ranar Litinin mai zuwa.

Sai dai bai fadi lokacin da za a bude layukan wayoyin hannu ba, wadda a cewar gwamnati 'yan ta'adda na iya amfani dasu.

Tun bayan da gwamnati ta sanar da soke 'yancin kan Kashmir din da mafi yawan al'ummarta musulmi ne, yankin ya cigaba da kasancewa cikin wani yanayi mai kama da dokar-hana-fita, daura da jami'an tsaro da ke cigaba da sintiri.