1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Zaben majalisar dokokin Jamhuriyar Benin

Suleiman Babayo ZMA
January 9, 2026

A kasar Jamhuriyar Benin ana ci gaba da shirye-shiryen karshe na zaben 'yan majalisar dokokin kasar, wanda ke zuwa wata guda bayan wani yunkurin juyin mulki a kasar da ke yankin yammacin Afirka.

Shugaba Patrice Talon  na Jamhuriyar Benin yana jawabi
Shugaba Patrice Talon na Jamhuriyar Benin yana jawabiHoto: Charles Placide Tossou/REUTERS

Ana ci gaba da shirye-shiryen karshe na zaben 'yan majalisar dokokin kasar Jamhuriyar Benin, wanda za a gudanar ranar Lahadi mai zuwa. Zaben yana zuwa watan daya bayan yunkurin juyin mulkin da wasu sojoji suka yi a kasar da ke yankin yammacin Afirka.

Zabe bayan yunkurin juyin mulki

Shugaba Patrice Talon na Jamhuriyar BeninHoto: Yanick Folly/AFP

Zaben majalisar dokokin zai iya nuna inda aka aka nufa a zaben shugaban kasa da aka tsara a watan Afrilu mai zuwa. Ana sa ran kawancen jam'iyyun da ke cikin gwamnatin Shugaba Patrice Talon zai taka rawar gani lokacin zaben na 'yan majalisar dokoki. Shi dai Shugaba Talon yana wa'adin karshe na mulkin shekaru 10, bayan lashe zabe sau biyu, na wa'adin shekaru biyar-biyar kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

Talon mai shekaru 67 da haihuwa hamshakin mai arziki ya taimaka wajen habaka tattalin arzikin kasar ta Jamhuriyar Benin cikin shekaru 10 da suka gabata. Amma ana zarginsa da tauye hakkin 'yan adawa a kasar.