SiyasaZambiya
Zambia ta dakatar da sanar da sakamakon zabe
August 14, 2026
Talla
Hukumar ta ce ta samu rahotannin sace takardun kada kuri'a a wasu wurare, a don haka za ta sake nazarin matakin dakatarwar cikin sa'o'i 24.
Kimanin mutane miliyan takwas ne suka yi rajistar kada kuri'a a Zambia, mai yawan al'umma kusan miliyan 22. Baya ga zaben shugaban kasa, ana kuma zaben 'yan majalisar dokoki da kansiloli a rumfunan zabe sama da 13,500.
Karin bayani : Yan Zambia sun yi zaben shugaban kasa
Masu sa ido sun ce an samu dogayen layuka da tsaiko a wasu rumfunan zabe, da kuma rudani kan jerin sunayen masu kada kuri'a.
Zaben na zama babban gwaji ga shugaba Hakainde Hichilema, wanda ke fuskantar dan takarar adawa Brian Mundubile, jagoran kawancen 'yan adawa da ke samun goyon bayan tsohon shugaban kasar Edgar Lungu.