1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zamfara: 'Yan bindiga sun kashe mutane da dama

Abdullahi Tanko Bala
January 9, 2022

Adadin mutanen da 'yan bindiga suka hallaka a wasu jerin hare hare da suka kai kauyukan Zamfara dake arewa maso yammacin Najeriya a cikin wannan makon sun kai mutum 200.

Symbolbild Nigeria Boko Haram
Hoto: Jossy Ola/AP Photo/picture alliance

Wata mai magana da yawun ministar taimakon jinkai Sadiya Umar Faruk ta baiyana takaici da hare haren wadanda ke tagaiyara rayuwar al'umma da tilasta musu barin muhallansu.

Wasu mazauna kauyukan Anka da Bukkuyum sun ce 'yan bindiga sun hallaka mutane akalla fiye da 140.

Sai dai gwamnan Zamfara Bello Matawalle ya ce mutane 58 ne aka kashe. Ya ce sarkin Anka ya bada sunayen mutane 22 da aka kashe yayin da Sarkin Bukkuyum ya bada sunayen mutane 36 da suka rasa rayukansu a hare haren.

A wannan makon gwamnatin Najeriya ta ayyana 'yan bindigar a matsayin 'yan ta'adda ta kuma ci alwashin daukar mataki domin murkushe su.