Zanga-zanga a Senegal ta kashe dalibi mai karatun likita
February 10, 2026
Hukumomi a Senegal sun tabbatar da mutuwar wani dalibi mai suna Abdoulaye Ba, da ke karatun likita, sakamakon arangama da 'yan sanda yayin zanga-zangar nuna fushi da rashin biyan alawus din dalibai.
Hatsaniyar ta barke ranar Litinin, a jami'ar Cheikh Anta Diop ta Dakar babban birnin kasar, inda dubban dalibai suka tada bore, nan da nan jami'an tsaro suka kutsa cikin makarantar, tare da tarwatsa taron da hayaki mai sa hawaye, yayin da daliban ke jifansu da duwatsu, kamar yadda hotuna da faya-fayan bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta suka nuna.
Karin bayani : Senegal ta ba wa hambararren shugaban Guinea-Bissau mafaka
Gwamnatin Senegal wadda ke fama da matsain tattalin arziki, ta mika sakon ta'aziyyarta ga iyalan mamacin, ta cikin sakon da mai magana da yawunta Marie-Rose Khady Fatou Faye ta fitar a wannan Talata.