Zanga-zangar malaman makaranta a Nijar
April 28, 2017Talla
Bayan kwanaki da aka kwashe ana kai ruwa rana tsakanin gwamnatin Nijar da dalibai, a yanzu kuma wata sabuwar ta kuno kai inda malaman makarantar suka sha alwashin kalubalantar gwamnatin a kan batun biyan albashi. Wanda malaman makarantar ke zargin gwamnatin da saba alkawarin da ta yi na biyan su kudaden albashin da suke bin gwamnatin bashi. Sai dai kuma an samu rarrabuwar kawuna a tsakanin malaman, yayin da wasu daga cikin malaman suka yi watsi da kiran da kungiyoyin suka yin na yin gangamin don yin Allah dai da gamnatin. Wannan dai ba shi ne karo na farko da irin haka take faruwa ba a Nijar.